Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

Date:

 

 

Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da bincike kan ƙorafin da wasu manoma ke yi na zargin shugabancin ƙaramar hukumar Tudun Wada karkashin jagorancin Hajiya Sa’adatu Yusha’u, kan kwace musu gonakinsu da ke Dajin Gurfa a karamar hukumar ta Tudun Wada a Kano.

InShot 20250309 102512486
Talla

‎Shugaban masu rinjaye na Majalisar Alhaji Lawan Hussain Cediyar ƴan Gurasa ne ya tabbatar da hakan jim kaɗan bayan amsa gayyatar da Majalisar ta yi wa kungiyar da ke rajin kare hakkin Ɗan-adam da tabbatar da daidaito a cikin al’umma wadda ta aike wa Majalisar korafin Manoman.

‎Da ya ke jawabi bayan amsa gayyatar da Majalisar ta yi musu, shugaban kungiyar Sa’id Bin Usman, ya ce akwai tarin korafe-korafe kan dambarwar hakkin mallaka na gonaki tsakanin shugabancin karamar hukumar Tudun Tada da kuma manoman yankin.

‎Manoma da dama ne a Dajin na Gurfa da ke yankin karamar hukumar Tudun Wada suka shigar da korafin su kan zargin shugabar ƙaramar hukumar da ƙwace musu Gonakin su, in da kuma suke fatan majalisar dokokin jihar kano da ta duba kokensu domin samar musu da adalci.

 

Freedom Radio

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya yi wa Buhari abun da Buharin ya kasa yi wa kakana- Jikan Shagari

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Nura Muhammad Mahe, jikan tsohon shugaban...

Yanzu-yanzu: Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga...

Gwamnatin Jihar Kano ta fara bincike kan mutuwar wasu ɗaliban makarantar Sakandare biyu

  Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Makoda, ya...

Kamfanin Yahuza Suya Ya aike da Sakon ta’aziyyar Rasuwar tsohon shugaban Kasa Buhari

Shugaban kamfanin Yahuza Suya and Catering Services Nig. Limited,...