Ban ce filin makarantar Bechi nawa ba ne, Kuma zan taimaka wajen gini Makarantar – Alh. Sagir Jaen

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

Biyo bayan koken da al’ummar garin Bechi dake karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano, da su ka yi ga gwamnan Kano Alh Abba Kabir Yusif na siyar da filin wata makarantar sakandiren mata dake yankin.

Yanzu haka Mamallakin filin da ake takardama akan sa a garin Bechi, Alhaji Sagir Isyaku Ja’en, ya bayyana asali yadda ya Mallaki filin a hannun wani Mutum Mai suna Farfesa Ibrahin Shehu, da shine ya siyar Masa da wajen, tun shekarar 2015, Kuma yana da cikakun takardun shedar mallaka daga kowace Hukumar da doka ta tanada.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Alhaji Sagir Ja’en, ya ce ya yi mamakin yadda ya ji mutane na korafi kan wannan fili, duk da cewa batun ya na gaban hukumomi don tantancewa, kuma ya kai dukanin wasu hujjoji domin tantance gaskiyar lamarin.

Wasu mutane na kokarin sayar da wata makaranta a Kano, al’ummar yankin sun nemi daukin gwamna Abba

Ya kara da cewa tun asali wannan gini da ake takardama akan sa na shedar ginin Makaranta, baya cikin gurin daya mallaka, kuma bai ce nasa bane, shi ma zai iya gina Makarantar domin al’umma su amfana” inji Alh Sagir.

Haka zalika Alh Sagir Ja”en ya yi kira ga al’ummar yankin su kwantar da hankalin su, Babu abin da zai taba ginin makarantar domin ba mallakinsa bane, kuma zai basu gudunmawar data kamata wajen gina Makarantar, Dalibai su yi karatu sosai.

InShot 20250309 102403344

“A karshe Alhaji Sagir Isyaku ya godewa al’ummar garin Bechi yadda suke kokarin kawo zaman lafiya,kwanciyar hankali, yana mai cewa insha Allahu zai tabbatar da kowa ya samu Nasara domin cigaban garin Bechi da kewaye.” Sagir Ja’en

Alhaji Sagir Ja’en ya kuma turowa kadaura24 wasu daga cikin shidar mallakar filin dake kusa da makarantar da ake takaddama akansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...

Gwamnatin Kano ta yabawa Tinubu saboda gyarawa da bude NCC DIGITAL PARK

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin jihar Kano ta yabawa Gwamnatin...