Gwamnatin jihar Kano za ta yi wata doka da za ta tilastawa kamfanoni masu zaman kansu daukar kashi 75 na maaijata yan asalin jihar.
A kan haka, gwamnatin ta kafa kwamitin kula da ɗaukar ma’aikata bisa ka’ida.
Da ya ke jawabi yayin wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a jiya Laraba a Kano, shugaban kwamitin, Dakta Ibrahim Garba, ya bayyana cewa za a mika daftarin dokar ga majalisar dokokin jihar da kuma gwamnan jihar domin amincewa.

Matakin, a cewarsa, na da nufin magance matsalar rashin aikin yi da kuma zaman kashe-wando tsakanin matasa a jihar.
Wasu mutane na kokarin sayar da wata makaranta a Kano, al’ummar yankin sun nemi daukin gwamna Abba
Malam Garba ya bayyana cewa Gwamna Abba Yusuf ne ya kafa kwamitin domin magance damuwar da ƴan jihar ke fuskanta dangane da yadda wasu kamfanoni masu zaman kansu su ke kin daukar ‘yan asalin jihar aiki.