Wasu mutane na kokarin sayar da wata makaranta a Kano, al’ummar yankin sun nemi daukin gwamna Abba

Date:

Daga Rabi’u Usman

 

Al’ummar ya garin Bechi dake cikin karamar hukumar Kumbotso sun koka akan yadda su ke zargin za’a kwace musu filin Makarantar Sakandaren ‘yan mata da Gwamnatin Kano Karkashin Ma’aikatar Ilimi ta fara gina musu Aji a cikin sa.

Kwamatin Samar da Cigaban yankin Bechi da kewaye (BECHI COMMUNITY DEVELOPMENT ASSOCIATION) ne su ka yi kira ga Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf akan Matakin da wasu Mutane da kawo yanzu ba’a san daga inda suke ba, suke kokarin yanka Filin (Awon Igiya) domin siyarwa Jama’a.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Inda suka ce, an samar da Filin ne tun lokacin mulkin tsohon Gwamnan kano Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso Zango na biyu a shekarar 2014 domin gina Makarantar Sakandaren ‘yan mata sakamakon Aron makarantar primary da a kayi.

Wanda primary din ake gudanar da ita daga wani lokaci da Safe zuwa wani lokaci a tashesu domin ‘yan sakandare su yi nasu Karatun.

Yanzu-yanzu: Kotu ta yi kwarya-kwaryar hukunci akan zargin rashawa da ake yiwa Ganduje da mai dakinsa

Sunce, Ma’aikatar Ilimi ta jihar kano ta amince da Gina Makarantar Sakandaren ‘yan mata a yankin tare da basu Cikakkiyar Shaidar fara ginin, wanda har an fara Gina aji guda amma daga bisani sai suka wayi gari ‘Dan kwangila ya kwashe kayan aikin sa ya tafi ba tare da an Sani ba.

Hakan ne ta sa wasu mutane su ka shiga yankin nasu suka fara yunkurin yanka Filin makarantar zasu fara saidawa jama’a a matsayin fulotai.

A hannu guda Suma, kwamatin Iyaye da Daliban makarantar primary da Sakandaren ‘yan mata a yankin Bechi ta Bakin Shugaban kwamatin SBMC Comrade Adamu Bechi, ya roki Mahukunta musamman gwamnatin kano tayi bincike akan yanda aka fara Gina Makarantar Sakandaren ‘yan matan amma aka Dakatar.

InShot 20250309 102403344

Wanda hakan ya janyo Babban kalubale ga makarantar da al’ummar yankin garin Bechi da kewaye na rashin samun Ilimin ‘yaya Mata.

A don haka su ka nemi daukin gwamnatin kano ta dubi halin da Ilimin ‘yaya Mata yake ciki a yankin nasu, wanda a cewar su, har Makobtan Unguwannin dake kewaye dasu suna zuwa makarantar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...

NUC ta kakabawa jami’o’i takunkumi kan yadda suke ba da digirin girmamawa a Najeriya

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) ta sanar...

Tsoffin Kwamishinonin Kano sun Musanta labarin goyon bayan Sanata Barau a 2027

Kungiya ta tsoffin kwamishinoni da suka yi aiki a...