Gwamnonin Nigeria na yunkurin dakatar da turawa kananan hukumomi kason kudadensu

Date:

 

 

Gwamnonin jihohin Nijeriya sun fara wani yunkuri na dakatar da shirin tura wa kananan hukumomin kasar kason kudaden su kai tsaye.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tsaiko wajen aiwatar da hukuncin kotun koli kan ‘yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi.

InShot 20250309 102403344
Talla

Wasu daga cikin gwamnonin da suka gana da shugaban kasa Bola Tinubu a ranar Talatar makon jiya, sun yi watsi da matakin babban bankin Nijeriya CBN na tura kudin kai tsaye, inda suka bayyana cewa ana bin kananan hukumomin tulin bashi.

Yanzu-yanzu: EFCC ta bayyana dalilan da su ka sa ta kama Jarumar Tiktok Murja Kunya

Majiyoyin jaridar Punch a fadar shugaban kasa sun ce, gwamnonin sun nemi shugaban da ya sake duba kan lamarin.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a shekarar da ta gabata ne Kotun kolin Nigeria ta tabbatar da yankin cin gashin kan kananan hukumomi a Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...