Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Date:

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi da tsohon Kwamishinan sa ido da tantance ayyukan gwamnatin Kano Muhammad Diggol sun gana da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau I. Jibrin a Abuja.

Ganawar wanda ta haɗa sauran masu ruwa da tsaki, ta mayar da hankali ne kan samar da ci gaba a Jihar Kano da kuma ciyar da ƙasa gaba.

InShot 20250309 102403344
Talla

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Barau ya wallafa hotunan ganawar da aka yi tare da bayyana muhimmancin haɗin gwiwa wajen samun ci gaba mai ɗorewa.

“Ci gaban jiharmu da ƙasa a kodayaushe yana kan gaba a ajandarmu, za mu ci gaba da haɗa kai da sauran masu ruwa da tsaki domin ciyar da jiharmu da ƙasa gaba,” in ji shi.

Kadaura24 a ruwaito cewa taron na daga cikin ƙoƙarin da shugabannin siyasa ke yi na yin cuɗanya da manyan mutane a ci gaban Jihar Kano da kuma yin aiki da manufa guda domin samun ci gaba

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...