Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) a hukumance, matakin da ke nuna sabon shiri na inganta ci gaban kasa.

Tare da rakiyar tawagarsa, Al-Mustapha ya isa hedkwatar jam’iyyar SDP da ke Abuja, inda shugabanni da magoya bayan jam’iyyar su ka tarbe shi da farin ciki. Shigarsa jam’iyyar na nuni da kudurinsa na jagoranci bisa adalci, tsaro, da ci gaba.

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Shugabannin SDP sun bayyana fatansu cewa Al-Mustapha zai karfafa manufofin jam’iyyar na hada kan kasa da samar da ingantaccen shugabanci.

Yayin da jam’iyyar ke ci gaba da fadada tasirinta, shugabanninta sun jaddada kudurinsu na gina tafiyar siyasa mai karfi da za ta canza alkiblar kasar nan.

InShot 20250309 102403344
Talla

Hamza Almustapha shi ne babban jami’in tsaron da ke kula da fadar shugaban kasa a zamanin Janar Sani Abacha.

Hamza Almustapha dai na daga cikin makusantan marigayi Janar Sani Abacha musamman a lokacin da ya yi shugaban Nijeriya na mulkin soja daga shekarar 1993-1998.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...

Shaye-shayen kwayoyi: Al’ummar Unguwar Rimin Kebe sun nemi agajin mahukunta

Daga Ibrahim Sani Gama   Kungiyar cigaban matasan unguwar Rimin Kebe...