Gwamnan jihar Rivers, Similanayi Fubara, ya bayyana cewa idan har aka samu karyewar doka da oda a jihar zai dora laifin hakan ga babban sufeto janar na ‘yansanda, Kayode Egbetokun.
Daily Trust ta rawaito yadda Fubara ya isa ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Rivers a cikin daren Juma’a don hana yunkurin sace kayayyakin zaben kananan hukumomi da za a gudanar a gobe Asabar a jihar.

Da yake jawabi a yayin taron manema labarai a birnin Fatakwal a ranar Juma’a, Fubara ya gargadi babban Sufeton ‘yansandan da ya kula da rawar da yake takawa a matsayin sa na shugaban rundunar ‘yansanda.
Gwamnan ya bayyana cewa babban aikin ‘yansanda shi ne kare lafiya da dukiyoyin al’umma, ba wai mamaye ofishin hukumar zabe ba.
Zaɓen ƙananan hukumomi: NNPP ta sauya dan takarar ciyaman a Kano
“Ina fadin wannan anan, IGP ya sani cewa duk wani abu da zai haifar da karya doka a wannan jihar, ina tunanin a karshe, ya shirya daukar alhakin hakan.

“Da safiyar yau, na samu rahotan tsaro dake cewa ‘yansanda sun mamaye ofishin hukumar zabe. Na yi matukar mamaki saboda kafin wannan lokacin na samu bayanin janye masu tsaron hukumar. Shi yasa naje wajen tunda mallakin gwamnatin jihar Rivers ne”