Gwamnatin Kano ta rabawa masu lalurar laka kayan sama da miliyan 7

Date:

Daga Rabi’u Usman

 

Gwamnatin jihar kano ta bayar da kayayyakin kula da kiwon lafiya ga masu larurar laka a nan jihar da kudin su ya tasamma sama da naira miliyan bakwai tare da basu tallafin kudi naira miliyan 1 domin gudanar da bikin zagayowar ranar masu larurar laka ta duniya.

Kwamishiniyar ma’aikatar mata, kananan yara da masu bukata ta musamman Hajiya Aisha Lawan Saji Rano ce ta bayar da kayayyakin ga Kungiyar masu larurar laka a shalkwatar ma’aikatar mata kananan yara da masu bukata ta musamman da yammacin ranar alhamis.

Talla

Kayayyakin da aka bayar sun hadar da keken zama (Wheel chair) guda 20, audugar mata, man tsabtace hannu, katata, bandeji da kayan dressing harma da zunzurutun kudi naira miliyan 1, da dai sauran su.

Bayan kammala taron ne wakilin mu ya zanta da kwamishina Aisha Lawan saji akan yanda aka gudanar da rabon kayan.

Kwankwaso ya karɓi yan APC sama da 960 zuwa jam’iyyar NNPP a Kano

Inda ta bayyana cewar, gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya sahale wa ma’aikatar ne domin mata, kananan yara da masu bukata ta musamman suma su san gwamnatin kano tana damawa da su.

Ta kara cewar, mutane da yewa musamman masu bukata ta musamman da masu larurar laka suna zuwa ma’aikatar suna ki koken su na rashin irin wadannan kayayyakin na amfanin yau da kullum.

Don haka gwamnan ya bayar da umarnin a samar musu da abinda ya sawwaka domin a rage musu radadin Damunar su.

Talla

A nasu bangaren Wasu daga cikin mutanen da suka amfana da tallafin musamman shugabancin Kungiyar masu bukata ta musamman bangaren masu larurar laka, sun bayyana Jin Dadin su sakamakon yanda suka ce sun dade suna neman me share musu hawaye akan damuwar su tare da neman wadannan kayayyakin amma basu da kudin Siya.

Talla

Sai ga shi rana tsaka gwamnatin kano ta biya musu bukatun su wanda suka dade suna nema.

A karshe sunce nan da 1 ga watan December zasu gudanar da bikin zagayowar ranar masu larurar laka wanda majalisar Dinkin Duniya take warewa sannan su baiwa mambobin Kungiyar musamman wadanda suke da bukata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...