RATTAWU NUJ da NAWOJ a Kano sun lashi takobin yi aiki tare

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kungiyar ma’aikatan radio da talabijin ta kasa reshen jihar kano RATTAWU ta ba da tabbacin hada kai da kungiyoyi NUJ da NAWOJ domin cigaban mambobinsu da jihar kano baki daya.

” Aikin mu iri daya ne kuma muna aiki tare to ya kamata mu shugabannin waɗannan kungiyoyi mu hada kan mu, mu dauka duk abun da ya shafi dayanmu ya shafemu duk, tabbas idan muka yi haka zamu sabi gagarumar nasara”.

Shugaban kungiyar ta RATTAWU reshen jihar Babangida Mahmoud Biyamusu ne ya bayyana hakan lokacin da ya jagoranci shugabannin kungiyarsu domin taya sabbin Shugabannin kungiyoyin NUJ d NAWOJ murnar lashe zabukan da suka yi a yan kwanakin baya.

Muhimmiyar sanarwa daga gwamantin jihar kano ga wadanda suka yi takara a NNPP

Ya ce idan shugabannin kungiyoyin suka cire ban-ban-bancen dake tsakanisu su za su samar da cigaba da mambobinsu da kuma jihar kano baki daya.

Shugaban na RATTAWU ya mika takardun taya murna ga sabbin Shugabannin NUJ d NAWOJ, Sannan ya horesu da su zamo masu gaskiya da rikon amana.

Da yake nasa jawabin shugaban kungiyar yan jaridu ta kasa reshen jihar kano Sulaiman Abdullahi Dederi ya godewa shugabannin na kungiyar RATTAWU bisa ziyarar taya murna da ya kai musu har Ofishinsu dake sakatariyar yan jaridu ta kano.

Talla

” Ina baka tabbacin za mu hada kai, kuma za mu yi aiki tare domin sai da hadin kai Sannan ake samun kowacce irin nasara, kuma dama da dan NUJ dana RATTAWU ko NAWOJ ko SWAN duk daya ne, kawai kundin tsarin mulkin kungiyoyin ne ya raba mu a wasu aiyukan, amma duk da haka zamu yi aiki tare don cigabanmu baki daya”. Inji shugaban NUJ na Kano.

Itama a nata bangaran shugabar Mata yan jaridu ta kasa reshen jihar kano Bahijja Malam Kabara ta ce wannan ziyarar wata yar manuniyace dake nuna cewa dukkanin kungiyoyin sun shirya yin aiki tare domin cigaban mambobinsu.

Bahijja kabara ta kara dace wa za su yi aiki kafada da kafada domin ciyar da aikin jarida gaba a jihar kano da kasa baki daya.

Haka kuma tayi kira da gwamnatin jihar kano da ta ci gaba da basu hadin kai yadda ya kamata badan komai ba sai don ganin an cigaba da bunkasa aikin ya jarida a jihar kano da kasa baki daya.

Ga hotunan yadda taron ya Kasance

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...