Masana sun fara sukar matakin gwamnatin Kano na soke jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Tsohon shugaban Jami’ar karatu daga gida ta Nigeriya wato (National Open University of Nigeria) Farfesa Abdullah Uba Adamu ya ce matakin da gwamnatin jihar kano ta dauka na soke jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi komawa baya ne ga kano da al’ummar jihar baki daya.

“Ba yadda za a yi ace wannan ci gaba ne, sai dai ace ci baya ne ga harkar ilimi, saboda idan aka ce duk gwamnatin da ta zo zata rushe cigaban da gwamnatin da ta gabace ta ta kawo, kawai saboda adawar siyasa to ba za a taba samun cigaba ba”.

Farfesa Abdullah Uba Adamu ya bayyana hakan ne a ga hira da yayi da gidan Radio freedom dake jihar kano a Arewacin Nigeria.

Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Yace kamata yayi gwamnatin jihar kano ta zauna da ga me yasa ita gwamnatin da ta gabata ta daga darajar Kwalejin zuwa jami’an, idan dalilan masu kyau ne sai a bata ta, idan babu wasu kwararan dalili sai a mayar da ita ta koma matsayinta na Kwaleji, amma idan akwai kwararan dalilai to bai kamata a dawo da jami’ar baya ba sabada adawar siyasa ba.

Talla

 

“Jihar Kano ta na da jami’o’i da dama yanzu, wannan jami’o’in irii-iri ne, akwai na gwamanti akwai masu zaman kansu, saboda talakawa ba su da wata jami’an da zasu yi tunkaho da ita kamar jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi, yanzu mayar da ita Kwaleji an kaskantar da ita an kuma kaskantar da ilimin da yara suke samu a cikinta”. Inji Farfesa Abdullah Uba Adamu

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito gwamnatin jihar kano ta ce ta dawo da jami’ar matsayinta na baya na Kwalejin horar da malamai, a yayin zaman majalisar zartarwar jihar wanda gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya jagoranta.

Gwamnatin baya ta Abdullahi Umar Ganduje ce dai ta daga likkafar Kwalejin zuwa jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...