NADDC za ta yi taron wayar da kai don haskawa matasa damammaki a harkar ƙera ababen-hawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar Kula da Ƙere-ƙere da Samar da Ababen-hawa ta Ƙasa, NADDC, da hadin gwiwa da Ofishin Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Cigaban Matasa, Sanya Ido da Aiwatar da ayyuka, na daf da yin wani gangamin taro na bajekolin fasaha da nufin haskawa matasa damammaki a ɓangaren ababen-hawa da sufuri a Nijeriya.

Taron, wanda za a gudanar a ranar 11 da 12 ga watan Satumba a Musa Yar’Adua Centre in Abuja, zai haska damammaki a ɓangaren sabuwar fasahar amfani da iskar gas a ababen-hawa, CNG, amfaninda wajen bunkasa tattalin arziki da kuma amfanin sa da tsari da yake da shi a ababen-hawa.

Yadda za ku sayi Shinkafar Tinubu akan Naira dubu 40 kowanne buhu

Mr. Rosilu Emmanuel, Mataimaki na Musamman kan dabarun aiki ga shugaban, NADDC, Mr. Oluwemimo Joseph, a wata sanarwa da ya fitar ya ce taron zai nunawa matasa hanyoyin samun arziki a bangaren ababen-hawa da sufuri.

Ya kara da cewa a taron, NADDC za ta ƙaddamar da gasar zanen ƙera mota mai amfani da iskar gas domin baiwa matasa damar bajekolin fasahar su da kuma karfafa musu gwiwa a fannin.

Yadda za ku sayi Shinkafar Tinubu akan Naira dubu 40 kowanne buhu

Ya kara da cewa “masu sha’awar shiga gasar za su aiko da faifain bidiyo na mintinan 2 zuwa 3 su nuna irin fasahar su a ciki zuwa addressing imel na naddcouncil@gmail.com daga ranar 1 zuwa 9 ga watan Satumba.”

Ya kara da cewa masana da masu ruwa da tsaki a harkar ƙere-ƙeren ababen-hawa da sufuri ne za su halarci taron.

Ya kara da cewa; Manyan baki da za su halarci taron sun hada da Bola Ahmed Tinubu, GCFR, Hon. (Dr.) Doris Uzoka-Anite, Ministan Kasuwanci da Masana’antu, Shugaban hukumar NADDC, Mr. Oluwemimo Joseph Osanipin, Mataimakin Shugaban ƙasa kan harkokin matasa, Hon. Titilope Gbadamosi, inda hakan zai kara wa matasa kaimi wajen cika burin su a fannin,” in ji sanarwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...