Mutane sun ƙi fita zaɓen ƙananan hukumomi a Bauchi

Date:

 

An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a wajen zaɓen ƙananan hukumomin da ke gudana a Jihar Bauchi.

Kamfanin Dillacin Labaran Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa zaɓen a ƙananan hukumomin Bauchi, Dass da kuma Tafawa Balewa, sun samu naƙaso yayin da mutane suka ƙi fitowa domin kaɗa ƙuri’a.

An fara zaɓen a wurare irin su Makarantar Sakandaren Gwallameji, Kofar Sarkin-Gwallameji, Makarantar Sakandaren Sa’adu Zungur da GSS Baba-Sidi, sai dai babu masu jefa ƙuri’a ba da yawa.

Yadda muka sha matsin lamba kan mu sa INEC ta soke zaɓen shugaban ƙasa na 2023 – Abdussalami

Masu jefa ƙuri’a da suka halarta sun hau layi cikin nutsuwa hankali, inda suka yi dakon zuwan jami’an zaɓe, wanda hakan ya bai wa jami’an hukumar damar gudanar da shirye-shiryensu cikin lumana.

NAN, ya ruwaito cewa an tura isassun jami’an tsaro a wuraren da ake gudanar da zaɓen, yayin da mafi yawan mazauna yankunan ke ci gaba da harkokinsu na yau da kullum.

An zargi Hadimin Gwamnan Kano da yada labarin karya kan ganawar Sanata Barau da tsaffin shugabannin LG

Wani rukuni na masu sanya ido kan zaɓen, sun bayyana jin daɗinsu game da yadda ake gudanar da zaɓen cikin lumana.

Mista Mamman Eri, babban mai sanya ido, ya yaba wa masu zaɓe, ma’aikatan zaɓe, da jami’an tsaro kan yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali.

Eri, wanda shi ne Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kogi (SIEC), ya jagoranci sauran Shugabannin Hukumar Zaɓe na Jihohi wajen sanya ido kan yadda zaɓen ke gudana.

“Mun zagayawa wurare da dama, zaɓen na gudana cikin kwanciyar hankali. Mutane suna gudanar al’amuransu yadda ya kamata, kuma akwai wakilan jam’iyyun

siyasa a wuraren zaɓen sun,” in ji Eri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...