An ƙayyade kuɗin fom din tsayawa takara a zaɓen ƙananan hukumomin Kano

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano (KANSIEC) ta ƙayyade kuɗin sayen fom ɗin tsayawa takara a zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a gudanar a bana.

Shugaban hukumar zaɓen, Farfesa Sani Lawal Malumfashi ne ya sanar da hakan ne a yayin bayyana jadawali da ƙa’idojin shiga zaɓen a wani taron manema labarai da hukumar ta gudanar a Kano a ranar Alhamis.

A yayin taron, hukumar zaɓen ta sanar da cewa duk mai son tsayawa takarar shugaban ƙaramar hukuma a zaɓen to zai sayi fom a kan naira miliyan 10.

A karon farko Farashin Kayan Abinchi ya sauka a Nigeriya

Yayin da ɗan takarar kansila kuma kuɗin fom ɗinsa ya kama naira miliyan biyar a cewar Farfesa Malumfashi.

Haka kuma, daga cikin ƙa’idojin shiga zaɓen dole ne ɗan takarar kujerar shugaban karamar hukuma ya kasance shekarun haihuwarsa sun kai 30 ko fiye, yayin da ɗan takarar kansila tilas ne ya kasance ya kai shekara 25 zuwa sama.

Yadda aka bankado haramtattun matatun man fetur 63 a Nigeria

Kazalika, Farfesa Malumfashi ya ce sai an yi wa kowanne ɗan takara a zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a yi gwajin ƙwaya kafin a ba shi damar tsayawa takara.

Daily Trust ta ruwaito cewa, hukumar zaɓe wadda ta yi gargadi kan gujewa duk wani lamari da zai tayar da hargitsi, ta ce za a buɗe ƙofar soma yaƙin neman zaɓe daga ranar 6 ga watan Satumba sannan a rufe a ranar 31 ga watan Oktoban bana.

Farfesa Malumfashi ya nanata cewa ba za su lamunci duk nau’i na rashawa ba kuma duk wanda aka samu da yunƙurin bayarwa ko karɓar cin hanci za a tona masa asiri sannan ya fuskanci hukuncin da aka tanadar.

Za a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar ne a ranar 30 ga watan Nuwambar 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...