Waɗanda Suka Yi Zanga-Zanga A 2012 Na Kokarin Danne Haƙƙin Yan Nigeria — Atiku

Date:

Daga Samira Ahmad

 

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki Gwamnatin Tarayya kan ƙoƙarin dakatar da zanga-zangar da aka shirya yi a ranar 1 ga watan Agusta.

Atiku ya bayyana yunƙurin da abun dariya, saboda waɗanda ke ƙoƙarin hana zanga-zangar su ne waɗanda suka yi wa tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan zanga-zanga a shekarar 2012.

Zanga-zangar, wadda matasa suka shirya, na da nufin jawo hankali kan ƙaruwar yunwa da wahala da ’yan ƙasa ke fuskanta.

Talla
Talla

Masu shirya zanga-zangar sun ce za a shafe kwanaki 10 duba da halin matsi da ke ƙara ta’azzara, wanda suka ce akwai buƙatar kulawar gaggawa daga gwamnatin tarayya da na jihohi.

A wani rubutu da ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook, Atiku ya jaddada cewa ‘yancin yin zanga-zanga yana cikin kundin tsarin mulkin Najeriya.

Kotu Ta Zauna Kan Shari’ar Kwankwaso Da EFCC

Ya buƙaci gwamnati da ta samar da yanayin tsaro da kwanciyar hankali don gudanar da zanga-zangar lumana, saboda ‘yan ƙasa suna da ’yancin gudanar da taro da bayyana ra’ayoyinsu.

Atiku ya soki gwamnati kan ƙoƙarin take waɗannan haƙƙoƙi, inda ya ce wannan ba ba ya cikin doka kuma yana barazana ga dimokuraɗiyya.

Ya ce gwamnati ya kamata ta mayar da hankali kan magance matsalolin da ke jawo yunwa da wahala maimakon ƙoƙarin hana zanga-zangar.

Idan ba a manta ba Shugaba Tinubu, ya roƙi ’yan Najeriya da su ƙaurace wa zanga-zangar tare da ba shi dama domin daidaita al’amura a ƙasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...