Kotu ta sanya ranar da Ganduje da Matarsa zasu bayyana a gabanta

Date:

Ana sa ran Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da matarsa Hafsat da wasu mutum shida za su bayyana a gaban kotu a Jihar Kano.

Ana sa ran za su bayyana a gaban kotun da ke tuhumarsu da almundahana a ranar Alhamis.

Ana zarginsu da cin hanci da almundahanar biliyoyin kuɗaɗe.

Gwamnatin Jihar Kano ta NNPP ce, ta shigar da su ƙara a gaban Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu.

Talla

A ranar 5 ga watan Yuni, kotu ta bai wa masu gabatar da ƙara izinin aike wa da waɗanda ake ƙara sammaci ta hanyar tallace-tallace ko jaridu, wanda kuma tuni aka wallafa a ranar 6 ga Yuni a jaridun Daily Trust da The Nation.

Abubunwan da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

Waɗanda ake ƙara su ne Abdullahi Umar Ganduje, matarsa Hafsat, Abubakar Bawuro, Umar Abdullahi Umar, Jibrilla Muhammad, kamfanin Lamash Properties Limited, Safari Textiles Ltd, da Lesage General Enterprises.

A zaman kotun da ya gabata, lauya mai kare wadanda ake tuhuma na shida, Nuraini Jimoh SAN, kaɗai ne ya halarci zaman kotun.

Sauran waɗanda ake ƙara, ciki har da Ganduje, ba su aike da wakilci ba.

Mai Shari’a Amina Adamu ta sanya ranar 11 ga watan Yuli domin ci gaba da shari’ar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Karyata Rahoton Cibiyar Wale Soyinka Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton da...

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Cire Maryam Sanda Daga Jerin Wadanda Za a Yi Wa Afuwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bada umarnin a...

Majalisar Kano ta buƙaci a soke ɗaukar aikin kwastam da aka yi a kwanan nan

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga dukkan...

‎ ‎Kuskure ne Tinubu ya cigaba da ciyo wa Nigeria bashi bayan ya cire tallafin mai – Sarki Sanusi

‎ ‎ ‎Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN),...