Hajjin bana: An kammala jigilar dawo da Alhazan jihar kano gida

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Da asubahin wannan rana ta laraba ne jirgin karshe dauke da Jirgin dauke da alhazan jihar kano ya sauka a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake kano.

Jirgin ya yi taso daga birnin Jeddah na kasar Saudiyya da misalin karfe 12:06 na safe, wanda hakan ke nuna an kammala dawo da alhazan jihar gida bayan kammala aikin hajjin bana.

Jirgin kamfanin Max Air da ya sauka a filin jirgin Mallam Aminu Kano da karfe 4:36 na safe, ya sauke alhazai 404 wadanda suka hada da jami’an gwamnati da mahajjata daga kananan hukumomi uku na kano:
1. Garun-Malam
2. Bebeji
3. Doguwa

Talla

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano tare da hadin gwiwar hukumar alhazai ta kasa NAHCON, sun tabbatar da gudanar da aikin dawo da su cikin kwanciyar hankali.

Abubunwan da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

Sanarwa da jami’an hulda da jama’a na hukumar jin dadin alhazai ta jihar kano Sulaiman Abdullahi Daderi ya aikowa kadaura24, yace Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya bayyana godiyarsa ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da mahukuntan Saudiyya, da ofishin jakadancin Nijeriya da ke Saudiyya, da kamfanonin jiragen sama da abin ya shafa, bisa goyon baya da hadin kai da suka ba su a lokacin gudanar da aikin hajji. .

Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya ce, “Mun ji dadin yadda dukkan alhazan mu suka gudanar da aikin Hajjinsu cikin nasara, kuma yanzu haka sun dawo gida lafiya, mun yaba da kokarin duk bangarorin da abin ya shafa wajen samun wannan nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...