Rikicin Masarautar Kano: Alkali Ya Hana Lauyoyin Magana da Jaridu

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Mai shari’a Amina Adamu Aliyu ta babbar kotun jihar Kano da ke zaune a sakatariyar Audu Bako, Kano, ta umurci lauyoyi a rikicin masarautu da su daina yin magana da manema labarai.

Alkalin kotun ta bayar da umarnin ne a lokacin da ake ci gaba da shari’ar, a ranar Alhamis.

Ta ce, “Umarni ne gare ku (lauyoyi) da kada ku sake yin wata hira da manema labarai kafin da kuma bayan yanke hukuncin kan dambarwar dake wanda ake kara na farko ya daukaka kara”.

Gwamnatin Kano ta cimma matsaya tsakaninta da yan kwangilar 5 kilomita a kananan hukumomin jihar

Daily trust ta ruwaito cewa jim kadan bayan wannan umarni, alkalin kotun ta tafi hutu domin yanke hukunci kan takaddamar.

Idan dai za a iya tunawa, Babban Lauyan Jihar Kano, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano da Majalisar Dokokin Jihar Kano, ne suka shigar da karar ta bakin Lauyan su Ibrahim Isah-Wangida, Esq.

Talla

Sun shigar da karar ne a ranar 27 ga Mayu.

A karar suna neman kotu ta hana Aminu Ado Bayero da sarakunan Bichi da Rano da Gaya da kuma Karaye cigaba da ayyana kansu a matsayin Sarakuna .

Karamar hukumar Wudil za ta tallafa Matasan da su ka sami aikin soja – Bilkisu Indabo

Wadanda suka amsa sun hada da Alhaji Aminu Ado-Bayero da Alhaji Nasiru Ado-Bayero Bichi Sarkin Karaye da Dr Ibrahim Abubakar ll da Sarkin Rano Alhaji Kabiru Muhammad-Inuwa da Alhaji Aliyu Ibrahim-Gaya Sarkin Gaya.

Sauran wadanda ake kara sun hada da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Darakta Hukumar DSS, Jami’an Tsaron Civic defense da rundunar Sojojin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...