Shin da Gaske Rikicin Masarautar Kano Ne Ya Hana Majalisar Dokoki Komawa Aikinta ?

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Majalisar dokokin jihar Kano ta musanta labarin da ake yadawa dake cewa ta ki dawo aiki ne saboda tsoron matsalar tsaro da ka iya tasowa saboda rikicin masarautar kano da ke ci gaba da faruwa a jihar.

Kakakin Shugaban Majalisar, Kamaluddeen Shawai ne ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya hakan a ranar Laraba, Inda ya ce “labarin bashi da tushe ballantana makama”.

Masu Garkuwa da Mahaifiyar Rarara sun Bayyana Abun da Suke Bukata Kafin su Sake ta

Shawai ya bukaci al’ummar jihar da su yi watsi da duk wani rahoton da ke nuni da cewa majalisar ki dawo wa aiki ne saboda rashin tsaro da rikicin masarautar ya haifar.

Talla

“Batun Jin tsoron ko kai hare-hare ga majalisar ba komai ba ne illa shafin gizo da wasu marasa kishin kano suke yadawa.

“Majalisar za ta dawo zamanta nan ba da jimawa ba,” in ji shi.

Ya nanata kudurin majalisar na yin aiki tare da Gwamna Abba Kabir-Yusuf domin ci gaban jihar baki daya.

Shawai ya bukaci al’ummar jihar Kano da su ci gaba da addu’ar samun zaman lafiya da hadin kai a jihar da kasa baki daya.(NAN)

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...