Shin da Gaske Rikicin Masarautar Kano Ne Ya Hana Majalisar Dokoki Komawa Aikinta ?

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Majalisar dokokin jihar Kano ta musanta labarin da ake yadawa dake cewa ta ki dawo aiki ne saboda tsoron matsalar tsaro da ka iya tasowa saboda rikicin masarautar kano da ke ci gaba da faruwa a jihar.

Kakakin Shugaban Majalisar, Kamaluddeen Shawai ne ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya hakan a ranar Laraba, Inda ya ce “labarin bashi da tushe ballantana makama”.

Masu Garkuwa da Mahaifiyar Rarara sun Bayyana Abun da Suke Bukata Kafin su Sake ta

Shawai ya bukaci al’ummar jihar da su yi watsi da duk wani rahoton da ke nuni da cewa majalisar ki dawo wa aiki ne saboda rashin tsaro da rikicin masarautar ya haifar.

Talla

“Batun Jin tsoron ko kai hare-hare ga majalisar ba komai ba ne illa shafin gizo da wasu marasa kishin kano suke yadawa.

“Majalisar za ta dawo zamanta nan ba da jimawa ba,” in ji shi.

Ya nanata kudurin majalisar na yin aiki tare da Gwamna Abba Kabir-Yusuf domin ci gaban jihar baki daya.

Shawai ya bukaci al’ummar jihar Kano da su ci gaba da addu’ar samun zaman lafiya da hadin kai a jihar da kasa baki daya.(NAN)

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...