Masu Garkuwa da Mahaifiyar Rarara sun Bayyana Abun da Suke Bukata Kafin su Sake ta

Date:

Yan bindigar da suka yi garkuwa da mahaifiyar shahararren mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara sun bukaci a biya kudin fansar ta Naira biliyan daya.

Majiyar Aminiya a kauyen Kahutu, inda aka yi garkuwa da Hajiya Hauwa’u Adamu, ya bayyana cewa masu garkuwar sun kira iyalan ta waya suna neman kudin tare da shaida musu cewa babu abin da ya same ta.

Majiyar, wadda ke da kusanci da iyalan dattituwar, ta ce ’yan bindigar “sun kira ne ta wayar wata ’yar gidan a lokacin da suka kai harin da suka sace Hajiya.

Talla

“Sun nemi a biya kudin fansa Naira biliyan daya, amma bayan tattaunawa da wani dan gidan suka rage kudin zuwa miliyan N900.

Da farko sun nemi tattaunawa ne da Rarara, amma kasancewar ba shi da lafiya tun bayan da suka sace ta, sai suka amince su yi magana da wani dan gidan.

Rikicin masarautar Kano: Abun da ya faru a zaman kotu na yau talata

“Sun tabbatar wa iyalan cewa Hajiya na cikin koshin lafiya kuma za su sake ta da zarar an biya kudin.

“ Cikin dan kankanin lokaci suka yi tattaunawar kuma har yanzu ba su sake kira ba.

“Amma duk hakan ina da yakikin ana ci gaba da tattaunawa da su.
“Iyalan na jiran ’yan bindigar su sake kira, a ci gaba da tattaunawa,” in ji majiyar, wadda ke da kusanci da gidansu Rarara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...