Tallafawa mata na taimakawa wajen gina kasa da cigaban al’umma – Kungiyar Matan Sojojin Ruwa

Date:

Daga Wasila Ladan

Kungiyar Matan Sojojin ruwa ta Nigeria (NOWA) ta bayyana baiwa mata tallafi domin su dogara da kawunan su, a matsayin hanyar gini al’umma da magance talauci a tsakanin al’umma.

Mataimakiyar shugabar kungiyar ta kasa Zainab Akpan ce ta bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a Abuja.

“Tallafawa mata yana da mahimmanci kuma zai taimaka wajen magance rikicin jinsi a cikin gidaje da kuma cikin al’umma. A halin da ake ciki a yau, tallafawa mata yana magance ƙalubalen talauci, rikicin jinsi a gidajensu da wuraren aiki, da ma cikin al’umma”. Zainab Akpan

Da dumi-dumi: Masu Tapswap sun daga ranar da zai fashe

Mrs Akpan ta ce tallafawa mata yana ba su damar ba da gudummawa sosai ga iyalansu, tattalin arzikin kasa, da kuma kara musu kima a idon duniya baki daya .

Talla

Ta kuma bayyana cewa tallafawa mata ya shafi muhimman abubuwa guda biyar na ci gaban mata: zamantakewa, tunani, ilimi, tattalin arziki da siyasa.

Zainab Akpan ta ce tallafawa mata na nufin karfafa al’umma, gina al’umma, samar da muhimmiyar alaƙa tsakanin matasa da maza a gida da kuma cikin al’umma, suna tasiri ga al’ummominsu.

Wakiliyar gidan rediyon Najeriya kuma sakatariyar kungiyar NAWOJ ta kasa Wasilah Ladan ta ruwaito Mrs Akpan ta ce tallafawa mata na basu kwarin gwiwar hidimtawa al’umma kamar yadda wasu mata suka yi tasiri sosai a cikin al’umma, matan da za a iya kafa misali da su a irin wannan fage su ne kamar su: Ladi Kwali, Amina J. Muhammed, Malala Yousafzai, Hajiya Fatima Kurfi, Ngozi Okonjo-Iweala, da kuma Dora Akunyili.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...