Rikicin Sarautar Kano: Yan Sanda Sun Dauki Bangare – Gwamnan Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mai magana da yawun gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya zargi rundunar ‘yan Sanda ta kasa reshen jihar da daukar bangaranci a Dambarwar Masarautar dake faruwa a jihar.

Idan za’a iya tunawa tun bayan da majalisar dokokin jihar kano ta rushe dokar da ta samar da karin masarauta 4 a jihar tare da dawo da Sarki Sanusi II a matsayin Sarkin Kano Ake ta dambarwa kan batun.

Hakan tasa sarki Aminu Ado Bayero ta dawo Kano, gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf ya umarci kwamishinan ‘yan sandan daya fidda sarki Aminu Ado bayero daga fadar sarkin ta gidan Rumfa.

Mai Kula da Mukullin Ka’aba Al-Shaiba ya Rasu

Sanusi Bature wanda shi ne daraktan yada labaran Gwamnan jihar Kano ya bayyana hakan ta cikin wata hira da tashar Talabijin ta Arise a ranar Juma’a.

Ya ce a matsayin gwamnan Kano na wanda kare rayuka da dukiyoyin al’umma ya rataya a wuyansa, Amma ya baiwa kwamishinan yan sandan jihar umarni har sau biyu yana bijirewa umarnin.

” Ba mu sani ba ko yan sanda za su mutunta umarnin da gwamnan ya basu game da Fitar da Aminu Ado Bayero daga gidan Sarki na Nasarawa domin yan sanda sun sauki bangaren a wannan dambarwa, basa karbar umarni daga gwamnan”. Inji Sanusi Bature

Yan Sanda Sun Fadi Matsayar su Kan Umarnin Gwamnan Kano na Fitar da Sarki Aminu Ado Daga Gidan Nasarawa

Ya ce bai dace yan sanda su rika bijirewa umarnin gwamna ba a matsayinsa na shugaban tsaro a jihar, ya kamata su bashi hadin kai ya sauke nauyin da kundin tsarin mulkin Nigeria ya ba shi.

Idan za a Iya tunawa kadaura24 ta rundunar ‘yan sandan bisa jagoranci CP Usaini Gumel tayi fatali da umarnin gwamnan na fitar da sarki Aminu Ado Bayero daga gidan sarki na Nassarawa, inda yace ba zasu bi umarnin ba saboda batun yana gaban kotu.

Ta cikin ganawar Sunusi Bature ya bayyana cewa hukuncin Kotun tarayya su ya bawa nasara domin kuwa kotun bata rushe dokar data sauke tsoffin sarakunan jihar guda biyar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya...

Aiyuka 5 da Gwamnan Kano ya yi alkawarin yi, bayan dakatar da rusau a Rimin Zakara

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci garin Rimin Zakara...

Shugaban K/H Garun Mallam zai Raba Audugar Mata 500 ga Makarantun Sakandiren Matan yankin

Daga Safiyanu Dantala Jobawa Shugaban karamar hukumar garun mallam Aminu...

Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...