Yadda Aka Shawo Kan Likitocin Asibitin Murtala dake Kano Suka Koma Bakin Aiki

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Shugaban kungiyar likitocin Najeriya NMA, ya yi kira ga mambobin kungiyar da su kwantar da hankalinsu, kuma wadanda ke aiki a asibitin kwararru na Murtala Muhammad dake Kano su koma bakin aiki ba tare da bata lokaci ba.

Hakan ya biyo bayan ganawar da sukai da shugaban asibitin, da babban sakataren hukumar kula da asibitocin Kano, kwamishinan lafiya, da kwamishinan ‘yan sanda, dangane da lamarin da ya faru a sashin masu haihuwa na asibitin.

Tun da farko, likitoci, ma’aikatan jinya, da sauran ma’aikata a asibitin sun kauracewa ayyukansu a asibitin don nuna adawa da harin da aka kaiwa wani abokin aikinsu.

APC da Yahaya Bello Sun Magantu Kan Neman Kujerar Ganduje

Rahotanni sun nuna cewa dangin wata mata mai juna biyu da ta mutu a lokacin tiyata ne, suka kai wa likitan da ke bakin aiki, inda suka yi garkuwa da shi na tsawon sa’o’i.

Marasa lafiya da suka ziyarci asibitin sun kasance cikin wani mawuyacin hali yayin da likitoci, ma’aikatan jinya, da sauran ma’aikata ba sa nan saboda fargaba.

Shugaban kungiyar likitocin Najeriya NMA reshen jihar Kano Dr. Sulaiman Abdullahi yayi karin haske inda ya bukaci gwamnatin jihar, ma’aikatar lafiya ta Kano, da hukumar kula da asibitocin jihar Kano (HMB), da jami’an tsaro, da duk masu ruwa da tsaki da su tabbatar da sun yi duk mai yiwuwa don kare lafiyar likitoci da sauran ma’aikatan jinya a asibitin.

Sabon Gwamnan Kogi Ya Zo da Sabon Salo a Dimokaradiyyar Nigeria

Babban Sakataren Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano (HMB), Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin da wasu suka kai wa wani likita a asibitin. Ya kuma bai wa likitocin da kungiyar su tabbacin tsaron lafiyarsu tare da yin kira ga hukumar da ta baiwa mambobinsu damar ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum a asibitin.

“Daraktocin hukumar, da hukumomin tsaro daga rundunar ‘yan sanda da DSS, da wakilan NMA, SSD, NGDP suka yi taron gaggawar, kuma an dauki matakan da suka dace. Wani bangare na matakin da aka dauka shi ne gurfanar da wadanda suka aikata laifin, domin za a dauki matakin shari’a kan duk wanda aka samu da laifi.

Har ila yau, za a karawa jami’an tsaron asibitin kaimi, da kuma kara yawansu a kofofin shiga da fita, da jami’an tsaro a wuraren da suka fi daukar hankali a cikin asibitin, da kuma kara wayar da kan jama’a kan yadda za a shawo kan matsalolin asibitoci.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...