Wutar Lantarki Ta Kashe Barawon Taransufoma

Date:

Wutar lantarki ta kashe wani barawon tiransufoma a unguwar Jattu da ke Karamar Hukumar Etsako ta yamma a Jihar Edo.

Al’ummar unguwar dai sun wayi gari ne da ganin gawar barawon da ake zargi, tana lilo a jikin turakun wutar lantarki da ke hada da tiransfomar.
Sai da wanda ake zargin ya yanke wayoyin da ka karkashin tiransufomar, ya ajiye su a gefe, sannan ya hau sama zai yanko dogayen wayoyin da ke raba wutar, inda a nan ne ya gamu da ajalinsa.
Shaidu sun bayyana cewa daga bisani jami’an Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Edo (BEDC) sun zo sun dauke gawar suka tafi da ita.
Kakakin ’yan sandan jihar, SP Chidi Nwabuzor, dai ya ce ba shi da labarin abin da ya faru.
Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Majalisar Zartarwa ta jihar Kano ta Amince da kashe Naira Biliyan 18 don aiwatar da wasu aiyuka

  Majalisar zartarwar jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir...

Gwamnatin Kano ta nemi majalisar dokokin jihar ta haramta auren jinsi

Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci majalisar dokokin jihar ta...