Wutar Lantarki Ta Kashe Barawon Taransufoma

Date:

Wutar lantarki ta kashe wani barawon tiransufoma a unguwar Jattu da ke Karamar Hukumar Etsako ta yamma a Jihar Edo.

Al’ummar unguwar dai sun wayi gari ne da ganin gawar barawon da ake zargi, tana lilo a jikin turakun wutar lantarki da ke hada da tiransfomar.
Sai da wanda ake zargin ya yanke wayoyin da ka karkashin tiransufomar, ya ajiye su a gefe, sannan ya hau sama zai yanko dogayen wayoyin da ke raba wutar, inda a nan ne ya gamu da ajalinsa.
Shaidu sun bayyana cewa daga bisani jami’an Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Edo (BEDC) sun zo sun dauke gawar suka tafi da ita.
Kakakin ’yan sandan jihar, SP Chidi Nwabuzor, dai ya ce ba shi da labarin abin da ya faru.
Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...

NNPPn Kano ta bayyana matsayar Kwankwaso kan batun yi wa Tinubu mataimaki a 2027

Shugabanin bangarori biyu na jam’iyyar NNPP a jihar Kano,...