Gwamnan Kano ya Bayyana Ranar da kashi na 2 na Daliban India da Uganda zasu tashi

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da gudanar da ayyuka da tsare-tsaren da za su inganta rayuwar al’ummar jihar.

Da yake jawabi a lokacin da yake duba ayyukan ofishin sa a cikin makonni 3 da suka gabata, a yayin da aka fara taron majalisar zartarwa ta jiha karo na 7 a gidan gwamnati da ke Kano, gwamnan ya ce an fara gudanar da ayyukan alheri da dama.

Talla

Ya bayyana cewa, a cikin wannan lokaci da gwamnatin ta yi nasarar kaddamar da rabon kayan abinci da suka hada da Shinkafa da Masara a mazabun jihar 484.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

PDP ta yi Maryani kan Hukuncin Kotun Kolin Nigeria

Ya kuma bayyana cewa gwamnati ta kuma kaddamar da rabon kayayyakin koyo da koyarwa, Uniform da jakunkuna/Takalmi, baya ga kaddamar da shirin kai dalibai karo na 1 da gwamnati ta dauki nauyin bayar da tallafin karatu a kasashen waje .

Bayan Hukuncin Kotun Kolin Nigeria, Tinubu ya Magantu

“Kashi na biyu na jigilar daliban da za su je Indiya za a ci gaba a ranar Juma’a, yayin da wadanda za su je Uganda za a kai su ranar Lahadi,” in ji gwamnan.

Hakazalika a cewarsa, gwamnati ta yi nasarar kaddamar da auren zawarawa da yan mata 1800 mai suna (Auren Gata) tare da bayar da tallafin kayayyakin daki, kayan abinci, tallafin kudi da sauran kayayyaki ga kowanne daga cikin ma’auratan da nufin tallafa musu.

Talla

Alhaji Kabir Yusuf wanda ya bayyana jin dadinsa ga al’ummar jihar bisa goyon baya da addu’o’i, ya kuma yabawa ‘yan jarida bisa goyon bayan da suke baiwa gwamnatinsa, tare da fatan ganin an hakan ya dore.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...