Da Dumi-Dumi: INEC ta Cire Sunan Dan Takarar Gwamnan Bayelsa na jam’iyyar APC

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Nigeria INEC ta cire sunan dan takarar APC Timpre Silva daga jerin sunayen ‘yan takarar gwamnan Bayelsa a zaben da za a yi a ranar 11 -11-23

Kadaura24 ta rawaito Hakan ta biyo bayan hukuncin kotu na farkon watan Oktoba da ya hana Silva tsayawa takara bisa hujjar an rantsar da shi gwamnan Bayelsa sau biyu duk da cewa shekaru 5 ya yi kacal.

Talla

Takardar sunayen yan takarar ta ƙarshe da INEC ta Sanya a shafin ta na internet tana dauke ne da sa hannun sakatariyar hukumar ta INEC Rose Oriaran Anthony.

Kwamitin Gwamnatin Kano na tantance ma’aikatan da Ganduje ya dauka aiki ya mika rahotansa

Yayin da aka fitar da jerin sunayen karshe na ‘yan takarar gwamna da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba, jam’iyyar APC ba za ta shiga zaben jihar Bayelsa ba sai dai idan kotu ta yanke hukunci kafin ranar zaben.

Gurbin sunayen dan takarar jam’iyyar APC da abokin takararsa, an bar shi babu komai bisa “umarnin kotu” .

Talla

Oriaran-Anthony, a cikin takardar da aka yi wa kwaskwarima, ya bayyana cewa matakin da hukumar ta dauka na yin biyayya ga umarnin kotu ne yasa ta cire sunan dan takarar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar...

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...