Musulunci ya Sami Karuwa ta hannan Kabiru Sani Kwangila Yakasai a Kano

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Wata Baiwar Allah ta karbi addinin musulunci karkashin jagoranci Shahararren dan kasuwar nan Alhaji kabiru sani kwangila Yakasai Khadimun Nabiyy.

 

Mrs Ekechi ta karbi addinin musulunci ne a wajan taron mauludin Annabi sallallah Alaihi wasallam na mako-mako da ake gabatar karkashin jagoranci khadimun Nabiyyi Alhaji kabiru sani kwangila Yakasai.

Talla

Elechi ta bayyana cewa ta yanke shawarar karbar addinin musulunci ne saboda ta fahinmci cewa shi ne addinin da Allah ya yarda dashi, kuma shi ne zai tseratar da mutum a rayuwar duniya da lahira.

Tace sun zo ne tare da tsohon mijinta wanda daman shi ya kasance musulmi ne, wanda ya dade yana kwadaitar da ita game da addinin musulunci wanda hakan yayi sanadiyar rabuwarsu, inda yanxu ta yanke shawarar karbar addinin musulunci.

Yadda Wani Saurayi Da Budurwa Suka Daurawa Kansu Aure A Jigawa

Sheikh Barrister Habib Muhammad Dan Almajir Fagge shi ne wanda jagoranci bata kalmar Shahada ya taya ta murna game da baiwar da Allah yayi mata na karbar addinin musulunci, sannan ya bayyana mata cewa yanxu ta zama kamar cikakkakiyar musulma kuma dukkannin Laifukan da tayi a baya Allah ya gafarta mata.

A Karshen Ekechi wadda ta bukaci a sanya mata suna Halima domin domin samun albarkacin. Ai suna kasancewar taji Tarihin wannan baiwar Allah, da irin gudunmawa da ita baya musulunci da musulmi.

Talla

Wakilinmu Kamal Yakubu Ali ya bamu labarin cewa Taron ya gudana a farfajiyar Gidan Alhaji munzali sani Musa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar...

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...