An ci tarar Kano Pillars Naira miliyan ɗaya

Date:

Daga Zainab Muhammad Kundila

 

Hukumar kula da gasar firimiya ta Nigeria a ranar Litinin ta ci tarar Kano Pillars kuɗi har Naira miliyan ɗaya, sakamakon kutsen da magoya bayantu suka yi a filin wasa, a wasan da suka fafata da Rivers United.

An tabbatar da cewa magoya bayan ƙungiyar Kano Pillars sun ketara shingen filin wasa domin murnar cin ƙwallon da suka yi a minti na 92 ​​a karawar da suka yi a filin wasa na Sani Abacha.

Talla

Bayan nazarin rahotanni daga jami’an wasan, hukumar kula da gasar Firimiya ta Najeriya, NPFL ta tuhumi kulob din da laifin karya doka mai lamba B13.18.

Yadda Wani Saurayi Da Budurwa Suka Daurawa Kansu Aure A Jigawa

Don haka an umurci kulob din da ya biya tarar cikin kwana 14 kuma ya ja kunne kan hakan, wanda gaza yin hakan zai zamo tamkar ci gaba da saɓa wa dokokin hukumar ta NPFL.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar...

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...