Kano Pillars ta baiwa Isa Jazino Muƙami

Date:

Daga Zainab Kabir Kundila

 

Kungiyar kwallon kafa ta Kano pillers ta nada ya tsohon kwararren dan wasan kwallon kafan Nigeria Isa Abdullahi Jazino a matsayin jami’in tuntuba na kungiyar.

 

Takardar nadin Mai dauke da sa hannun Shugaban kungiyar Mahmud Babangida, ta ce an nada Isa Abdullahi Jazinon ne Saboda ana ganin akwai gagarumar gudunmawa da zai iya baiwa kungiyar don ta kai ga nasara a wasannin ta.

Talla

” Muna fatan zaka yi amfani da kwarewar da kake da ita wajen bamu shawarwarin da zasu kara bunkasa kungiyar, musamman a wasannin za ta buga a nan gaba.

Shugaban NNPP na kasa, Farfesa Alkali ya yi murabus

Isa Abdullahi Jazino kwararren dan wasan kwallon kafa ne da ya buga wasanni a kungiyoyin kwallon kafa da dama a ciki da wajen Nigeria sama da shekaru 25 da suka gabata.

Alƙaliyar Kotun Sauraren Kararrakin Zabe a Kano ta Koka bisa yunkurin wani Babban Lauya na bata cin-hanci

Sabon jami’in tuntubar ya kuma taba zama dan wasa a Kano Pillars da wasu kungiyoyi a Nigeria, sanann ya taba bugawa Nigeria wasa don haka ana ganin zai bada gudunmawa sosai wajen ciyar da kungiyar kwallon kafa ta Kano pillers gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu ya ba da Umarnin rage kudin aikin Hajjin 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya umarci hukumar kula...

Hukumar yaƙi da cin-hanci ta jihar Kano ta fara binciken Ganduje kan zargin karkatar da Naira biliyan 4 a Kano

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da...

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics ta Yi Allah-wadai da Yunkurin Siyasantar da Bikin Cikar Najeriya Shekara 65 a Kano

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics (FPA) ta yi Allah-wadai...

Yan Uwa da Abokan Arzikin Sabon Kwamishinan Shari’a na Kano Sun Shirya masa addu’o’i na musamman

Yan uwa da abokan arziki na kwamishinan shari'a na...