Zamu haɗa hannu da ma’aikatar Shari’a ta kano don ladaftar da masu karya dokokin hukumar tace fina-fina – Abba El-Mustapha

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

 

Hukumar tace Fina-finai da dab’i ta jihar Kano tace zata hada hannu da ma’aikatar shari’a ta Kano domin ladaftar da masu karya dokokin hukumar dan a tsaftace harkar Masana’antar tare da kawo mata cigaba mai dorewa.

 

“Na zo ma’aikatar shari’a ne dan na kawo muku kwafin sababbin dokokin da hukumarmu take so ta kara tare da zamanantar da tsofaffin dokokin da take aiki dasu domin suyi dai-dai da zamani da ake a ciki yanzu”. Abba El-Mustapha

Talla

A sanarwar da jami’in hulda da jama’a na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, yace shugaban hukumar tace fina-finan Abba El-Mustapha ne ya bayyana haka a yayin wata ziyarar taya murna tare da karfafa alaka a tsakankanin hukumomin Biyu.

Kwankwaso ya Taya Ganduje Murnar zama Shugaban APC na Ƙasa

Shugaban hukumar tace fina-finan ta kano yace mafi yawan dokokin da hukumar take aiki dasu a halin yanzu na bukatar sauyi ko kuma ayi musu gyara don su dace da wannan zamanin

Shi ma anasa jawabin Kwamishinan ma’aikatar Shari’a ta jahar Kano, Barr. Haruna Isah Dederi ya yabawa Shugaban hukumar tace fina-finan Abba El-mustapha dan gane da kokarin da yake naganin hukumar ta cimma wani mataki wanda zai bunkasa aiyukan hukumar.

Talla

“Kofar mu abbude take domin bayar da dukkan shawarwarin da zasu taimaki hukumar tace fina-fina domin sabuntawa da samar da dokokin da zasu kara inganta aiyukan hukumar”. Inji Dederi

Kwamishinan ma’aikatar Shari’ar ta kano, ya kuma nuna farin cikin sa dangane da ziyarar da Alh. Abba El-mustapha ya kai musu a matsayin sabon Shugaban hukumar tace fina-finai da dab’i ta jahar Kano domin jaddada alaka tare da neman yin aiki tare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...