Bankwana: Gwamna Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa.

 

” Na yafewa duk wanda ya taba fadar wata magana akai na , Kuma nima Ina rokon ku da ku yafe min duk laifukan da nayi muku, tunda dama Malam yanzu ya fadi muhimmancin yafiya a addinin musulunci”. Ganduje

 

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da ya halarci Tafsirin Al’qur’ani mai girma a masallacin juma’a na alfur’qan dake Nasarawa GRA kano.

 

” Wa’adina ya zo ƙarshe a mulkin jihar kano Ina yi muku bankwana, ina yi muku fatan alkhairi, kuma wadanda muka batawa ku yafe mana, nima na yafewa duk wanda ya fadi wani abu akai na ko meye na yafe masa” . Ganduje ya jaddada

Ganduje dai ya mulki jihar kano tsahon shekaru 8 tun daga Shekara ta 2015 zuwa ƙarshen watan gobe 29 ga watan mayun 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...