Bankwana: Gwamna Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa.

 

” Na yafewa duk wanda ya taba fadar wata magana akai na , Kuma nima Ina rokon ku da ku yafe min duk laifukan da nayi muku, tunda dama Malam yanzu ya fadi muhimmancin yafiya a addinin musulunci”. Ganduje

 

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da ya halarci Tafsirin Al’qur’ani mai girma a masallacin juma’a na alfur’qan dake Nasarawa GRA kano.

 

” Wa’adina ya zo ƙarshe a mulkin jihar kano Ina yi muku bankwana, ina yi muku fatan alkhairi, kuma wadanda muka batawa ku yafe mana, nima na yafewa duk wanda ya fadi wani abu akai na ko meye na yafe masa” . Ganduje ya jaddada

Ganduje dai ya mulki jihar kano tsahon shekaru 8 tun daga Shekara ta 2015 zuwa ƙarshen watan gobe 29 ga watan mayun 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...

Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

    Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da...

Tinubu ya yi wa Buhari abun da Buharin ya kasa yi wa kakana- Jikan Shagari

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Nura Muhammad Mahe, jikan tsohon shugaban...

Yanzu-yanzu: Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga...