Ƴan sanda sun kama waɗanda ake zargi da yunkurin ƙona ofishin INEC a Kano

Date:

Rundunar ƴan sanda a Kano ta ce ta kama mutum huɗu da ake zargi da yunkurin ƙona ofishin hukumar zaɓe a karamar hukumar Takai na jihar.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun ƴan sandan jihar SP Abdullahi Kiyawa ya fitar, ta ce ana zargin mutanen huɗu da yunkurin ƙona ofishin na INEC a daidai lokacin da ake sanar da sakamakon zaɓe.

BBC Hausa ta rawaito Sanarwar ta ce ƴan sandan sun samu nasarar kama mutanen ne bayan kai samamen gaggawa tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro.

Haka ma, ƴan sanda sun ce wasu ƴan bangar siyasa sun kai hari kan ofishin yakin neman zaɓe na jam’iyyar NNPP a karamar hukumar Tudun Wada, inda aka kashe mutum biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zabe:An kama ƴandaba sama da 100 da ake zargi da yunkurin tada tarzoma a Kano – INEC

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta...

Gwamnan Bauchi ya nada ɗan ƙasar China a matsayin mai bashi shawara kan tattalin arziƙi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya nada Mista Li...

Gwamnati da Malamai a Kano sun fitar da mafi karanci kudin sadaki da Zakka da Diyar Rai

Daga Kamal Yakubu Ali   Hukumar Zakka da Hubusi da Takwararta...