Ƴan sanda sun kama waɗanda ake zargi da yunkurin ƙona ofishin INEC a Kano

Date:

Rundunar ƴan sanda a Kano ta ce ta kama mutum huɗu da ake zargi da yunkurin ƙona ofishin hukumar zaɓe a karamar hukumar Takai na jihar.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun ƴan sandan jihar SP Abdullahi Kiyawa ya fitar, ta ce ana zargin mutanen huɗu da yunkurin ƙona ofishin na INEC a daidai lokacin da ake sanar da sakamakon zaɓe.

BBC Hausa ta rawaito Sanarwar ta ce ƴan sandan sun samu nasarar kama mutanen ne bayan kai samamen gaggawa tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro.

Haka ma, ƴan sanda sun ce wasu ƴan bangar siyasa sun kai hari kan ofishin yakin neman zaɓe na jam’iyyar NNPP a karamar hukumar Tudun Wada, inda aka kashe mutum biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...