INEC ta fara karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da jihar Ekiti

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Jihar Ekiti da ke kudu mao yammacin Najeriya ta kasance jiha ta farko da ta fara gabatar da sakamakonta na zaben shugaban ƙasar da aka gudana ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu.

Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood ya bayar da dama ga babban jami’in haɗa sakamakon zabe a jihar ta Ekiti domin gabatar da sakamakon a zauren tattara sakamakon dake Abuja

Babban jami’in lura da zaben jihar ta Ekitin ne ya jagoranci gabatar da sakamakon kamar haka:

APC – 201,494

PDP – 89,554

LP – 11,397

NNPP – 264

SDP – 2011

Sakamakon ya nuna cewa jami’iyyar APC ce ta samu nasara a zaɓen na jihar Ekiti.

Sai dai babban jami’in hada sakamakon zaɓen ya ce an soke zabe a wasu mazaɓu biyu saboda wasu matsaloli guda biyu da suka hadar da:

Tangardar na’urar BVAS

Da kuma samun adadin mutanen da suka kada kuri’a a mazabar ya zarta adadin mutanen da na’uar BVAS ta tantance

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace...

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi al'ummar jihar Kano...

2027: Shugabannin APC a Kano ta Kudu sun mika bukatarsu ga Sanata Kawu Sumaila

Shuwagabannin jam’iyyar APC da Sakatarorin su na mazabar Kano...

Tinubu ya sake ƙaddamar da aiki titin Abuja zuwa Kaduna

Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gina...