INEC ta fara karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da jihar Ekiti

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Jihar Ekiti da ke kudu mao yammacin Najeriya ta kasance jiha ta farko da ta fara gabatar da sakamakonta na zaben shugaban ƙasar da aka gudana ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu.

Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood ya bayar da dama ga babban jami’in haɗa sakamakon zabe a jihar ta Ekiti domin gabatar da sakamakon a zauren tattara sakamakon dake Abuja

Babban jami’in lura da zaben jihar ta Ekitin ne ya jagoranci gabatar da sakamakon kamar haka:

APC – 201,494

PDP – 89,554

LP – 11,397

NNPP – 264

SDP – 2011

Sakamakon ya nuna cewa jami’iyyar APC ce ta samu nasara a zaɓen na jihar Ekiti.

Sai dai babban jami’in hada sakamakon zaɓen ya ce an soke zabe a wasu mazaɓu biyu saboda wasu matsaloli guda biyu da suka hadar da:

Tangardar na’urar BVAS

Da kuma samun adadin mutanen da suka kada kuri’a a mazabar ya zarta adadin mutanen da na’uar BVAS ta tantance

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

PDP ta yi watsi da zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono dake Kano

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya...

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zabe:An kama ƴandaba sama da 100 da ake zargi da yunkurin tada tarzoma a Kano – INEC

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta...

Gwamnan Bauchi ya nada ɗan ƙasar China a matsayin mai bashi shawara kan tattalin arziƙi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya nada Mista Li...