Wike Ya Yi Barazanar Hana Atiku Wurin Kamfen A Ribas

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya yi barazanar soke amincewar da yayi na bada filin wasa na Adokiye Amiesimaka da ke Fatakwal, domin gudanar da taron yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar.

 

Wike ya ce babban daraktan kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jihar, Dr. Abiye Sekibo, ya kasance yana yawan ziyartar wurin taron wata guda kafin ranar 11 ga watan Fabrairu da aka basu domin gudanar da taron.

 

Talla

Gwamnan ya bayyana cewa sun amince Atiku Abubakar ya gudanar da taron ba tare da sun biya ko sisin kwabo ba, amma daraktan yaƙin neman zaben Atikun na Ribas yana ta sintiri a filin bayan kuma za’a basu filin wasa ne sa’o’i 48 kafin taron.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Wike, wanda ya bayyana hakan a ranar Juma’a a lokacin da yake jawabi a taron kaddamar da yakin neman zaben jam’iyyar PDP reshen jihar Ribas a karamar hukumar Oyigbo, ya ce Sekibo ba shi da hurumin yin sintiri a filin wasan wata daya kafin ranar da aka kayyade.

 

Wike ya gargadi Sekibo da kada ya harzuka gwamnatin jihar Ribas ta janye amincewar da akai na basu filin wasan na jihar makonni kadan kafin zuwa ranar da zasu gudanar da yakin neman zabe, in ba haka ba za a soke amincewar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Likitocin Jinya da Ungozoma sun janye yajin aiki – Ministan lafiya

Ƙungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta...

Sarkin Hausawan Arewa, Amb. Balarabe Tatari, Ya Aike da Sakon Ta’aziyyar Buhari da Dantata

Sarkin Hausawan Arewa kuma Ambasadan Zaman Lafiya, Alhaji Balarabe...

INEC ta sanya ranar fara rijistar masu zabe a Nigeria

Hukumar zaɓen Najeriya ta ce nan gaba cikin wannan...