Wasu mahara sun sace kwamishinan gidaje da raya karkara na jihar Benuwe, Ekpe Ogbu.
Mai taimaka wa gwamnan jihar kan tsaro kanar Paul Hemba ya tabbatar wa kafar talabijin ta Channels cewar an sace Mr Ogbu da yammacin ranar Lahadi a mahaɗar Adankari kan hanyar Otukpo-Ado.

Ya tabbatar da cewa an gano motar da kwamishinan ke ciki a lokacin sace shi, kuma tuni jami’an tsaro suka fara bincike.
Sai dai ya ce ba a samu wani labari daga waɗanda suka sace shi ba.