Ƴan gida ɗaya su 6 sun mutu bayan cin abinci da tsaka ta saka baki

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Wasu ƴan gida ɗaya su shida sun mutu bayan da aka ce sun ci abinci da ake zargin tsaka ce ta sa baki a unguwar Mowe da ke karamar hukumar Obafemi Owode a jihar Ogun.

Wadanda su ka rasun, da su ka haɗa da Adeleke John Samuel, wani akawun hayar, matarsa, Pamela Adeleke, ‘ya’yansu biyu da wasu ‘yan uwansu biyu, an gano gawarwakinsu ne da sanyin safiyar Juma’a, kamar yadda rahoton jaridar TheEagle Online ya bayyana.
Rahoton ya kara da cewa lamarin ya faru ne a lokacin da Lawal Ojo, mai gadin gidan ya yi zargin akwai wata matsala bayan da ya ji gidan ya yi tsit da safe ba kamar yadda aka saba jin hayaniya ba.
Talla
“Ya sanar da makwabtansu, inda su ka kutsa cikin gidan sai kawai suka ga gawarwakinsu a dakuna daban-daban,” in ji rahoton.
“Dukkan su suna cikin yanayin barci, in ji majiyar, wanda ke nuni da cewa watakila sun mutu a cikin barcinsu.”
A cewar rahoton, Ifenatuora Ijeoma, wacce ta shaida lamarin, ta ce mai yiwuwa sun ci gubar ne a lokacin da su ka ci abincin dare.
Ta tabbatar da cewa, bayan da aka duba kayan kicin din, an ga wata matacciyar tsaka a cikin tukunyar miya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Likitocin Jinya da Ungozoma sun janye yajin aiki – Ministan lafiya

Ƙungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta...

Sarkin Hausawan Arewa, Amb. Balarabe Tatari, Ya Aike da Sakon Ta’aziyyar Buhari da Dantata

Sarkin Hausawan Arewa kuma Ambasadan Zaman Lafiya, Alhaji Balarabe...

INEC ta sanya ranar fara rijistar masu zabe a Nigeria

Hukumar zaɓen Najeriya ta ce nan gaba cikin wannan...