Mun Kafa Kungiyar TNM ne don ceto Nigeria daga Mawuyacin halin da ta ke ciki – Kwankwaso

Date:

 

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na jagorantar wani gagrumin taro na wasu manyan siyasar Najeriya karkashin wani yunkuri mai suna The National Movement TNM.

Fitattun mutane da ƴan siyasa da suka halarcitaron sun haɗa da Alhaji Tanko Yakasai da Capt Idris Wadatsohon gwamnan Kogi da Rufai Alkali da Aminu Ibrahim Ringim tsohon dan takarar gwamna a jihar Jigawa da kuma Inijiniya Buba Galadima.

A jawabin Kwankwaso ya ce wasu ƴan Najeriya ne da suka damu da abin da ke faruwar suka haɗa kai don ceto ƙasar daga mawuyacin halin da ta shiga.

Ya ce yunƙuri ne na ƴan Najeriya masu kishi da suke zaune a gida da kasashen waje.

A cewarsa za su duƙufa wajen farfaɗo da tattalin arzikin kasar da inganta rayuwar ƴan kasa a birni da karkara

Ya ce sun shirya tsaf domin tunkarar matsalar tsaro da ta addabi Najeriya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...