Abba kyari ya musanta zargin safarar Muggan kwayoyi

Date:

Babban jami’in ‘yan sandan Najeriya da aka dakatar ya musanta zargin alakanta shi da kungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ta ƙasa da ƙasa.

An kama Abba Kyari ne a makon da ya gabata bayan da hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasar NDLEA ta zarge shi da alaƙa da wata kungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi da ke aiki tsakanin Najeriya da Habasha da kuma Brazil.

Sai dai a ranar Litinin ya shaidawa wata kotu a Abuja babban birnin kasar ta hannun lauyoyinsa cewa ƙirƙirar zargin aka yi.

Hukumar NDLEA ta yi zargin cewa Mista Kyari ya yi yunkurin bai wa jami’anta cin hanci don kilo 25 na hodar ibilis da jami’ansa suka kama sannan suka raba.

Amma ya musanta zargin.

Ya ce jami’an hukumar NDLEA ne suka masa gadar zare bayan ya nace sai an bayar da lada ga wanda ya bayar da labarin da ya kai ga kama waɗanda ake ake zargi da safarar miyagun kwayoyi kamar yadda suka amince da farko.

Ɗaya daga cikin lauyoyinsa Hamza Nuhu Dantani, ya shaida wa BBC cewa sun kuma gabatar da bukatar neman belinsa.

Ya ce saboda an ci gaba da tsare shi sama da sa’a 24 ba tare da gabatar da shi kotu ba kan zargin da ake masa, wanda ya saɓa ƴancinsa na ɗan adam.

A ranar Alhamis kotu za ta saurari buƙatar da lauyoyinsa suka shigar na neman beli.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...