An ritsa ƴan bindiga a gidan gyaran hali na Jos bayan da su kai yunƙurin ɓalle shi

Date:

 

Ƴan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai hari gidan gyaran hali da ke Jos, Jihar Filato.

Francis Enobore, kakakin gidan gyaran halin ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a jiya Lahadi.

Ya ce ƴan bindigan sun dira a ƙofar shiga gidan gyaran halin ne da misalin ƙarfe 5:20 na yamma, inda su ka nufi babbar ƙofar shiga.

Su na dosar ƙofar, in ji Enobore, sai su ka buɗewa ma’aikatan gurin wuta, su ma kuma su ka maida martani, inda a hakan ne ƴan bindigar su ka samu damar ɓalle ƙofar su ka shiga harabar gidan.

Bayan sun samu shiga cikin gidan, ai kuwa sai a ka ritsa su bayan da a ka gaiyato sauran jami’an tsaro su ka yi wa gidan gyaran halin ƙawanya, in ji Enobore.

Daily Nigeria ta rawaito Enobore ya ƙara da cewa an kuma ƙaro dakaru da ga shalkwatar gidajen gyaran hali.

Ya ƙara da cewa yanzu dai an shawo kan lamarin, bayan da gamaiyar jami’an tsaro da a ka girke a wajen su ka mamaye gidan gyaran halin kuma sun fi ƙarfin ƴan bindigan.

Yayin da ƴan bindigar su ka shiga halin ƙaƙa-ni-ka-yi, Enobore ya sanar da cewa za a ci gaba da bada bayanai da zarar an wasu wani ci gaba a bisa lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...