FAAN ta dakatar da wasu ma’aikata bisa zargin karɓar na-goro a hannun matafiyi

Date:

 

Hukumar kula da Filayen Jirgin Sama ta Ƙasa, FAAN ta sanar da dakatar da wasu ma’aikatanta bisa zargin karɓar na-goro a hannun wani matafiyi a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Jihar Legas.

Janar-Manaja mai kula da sashin Hulɗa da Jama’a, Henrietta Yakubu ce ta baiyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a yau Asabar a Legas.

Ta baiyana cewa wannan matakin dakatarwar da a ka ɗauka wani yunƙuri ne na kakkaɓe ɓata-garin ma’aikata da cin hanci a filin jirgin saman na ƙasa.

Yakubu ta ce ma’aikatan da abin ya shafa sun haɗa da na ɓangaren tsaron filin jirgin sama, AVSEC da kuma na ɓangaren kula da kwastomomi, inda ta ƙara da cewa dukkansu an dakatar da su.

Daily Nigeria ta rawaito Janar-Manaja ɗin ta ƙara da cewa an ɗauki matakin ne domin ya zama darasi ga sauran ɓata-gari na hukumar, waɗanda ba su da wani aiki sai na zubar da mutuncinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...