Zaben APC: Bamu Sami korafi ko daya ba a Kano – Kwamitin APC

Date:

Daga Sani Danbala

 

Kwamitin karbar korafe-korafen zaben Shugabannin jam’iyyar APC da aka gudanar anan kano yace yazuwa Wannan Lokaci babu Wani korafi da Suka karba Dangane da zaben da aka gudanar a filin Wasa na Sani Abacha dake Kofar mata.

Shugaban Kwamitin Dr Tony Macfoy ne ya bayyana hakan Yayin Wata ganawa da sukai da Manema labarai a helkwatar jam’iyyar APC ta Jihar Kano.
Dr. Macfoy Wanda daka Kwamitin yace Rashin Samun korafi akan wancan zaben daga ko Mutum daya ya nuna cewa kowa ya Amince da yadda aka gudanar da zaben .
” mun yi Zama na kusan kwanaki uku, Amma har yanzu Babu ko Mutum daya daya Zo domin Mika Rahoton korafinsa”.
Sai dai Shugaban Karamar yace zasu je hutun Rabin Lokaci ,Inda zasu fara rubuta Rahotonsu domin mikawa ga uwar jam’iyyar APC ta Kasa dake Abuja .
“Muna nan kano har Ranar asabar Mai zuwa ,Kuma duk Wanda Zai Kawo korafi game da zaben a Shirye Muke mu karba Kamar yadda kundin tsarin Mulkin jam’iyyar APC ya tanada”.
Kwamitin Mai Mutane 5 ya Fara Zaman karbar korafe-korafen ne tun Ranar asabar din data gabata a helkwatar jam’iyyar APC ta kano dake kan titin maiduguri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...