Maulidi : Mataimakin Gwamnan Kano yayi kira da al’ummar Kasar nan su zauna lafiya da juna

Date:

Daga Nura Abubakar
 Mataimakin gwamnan jihar Kano Dr.Nasiru Yusuf Gawuna ya yi kira da a zauna tare a zauna lafiya tsakanin al’ummar kasar nan.
 Ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadin nan a Abeokuta, Jihar Ogun yayin bikin mauludi na  Karo na 55 da Kungiyar Musulunci ta Attoreeqatul Qadiriyya Al-Azeeziyah ta shirya don murnar zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam).
 Ya yi kira da a zauna lafiya, tare da nuna kauna, hakuri da Sauran kyawawan dabi’u ga al’umma domin haka addinan Musulunci ya koyar.
Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Mataimakin Gwamnan Hassan Musa Fagge ya aikowa Kadaura24 yace Dr. Gawuna ya roki Musulmai da su sanya hadin kai, kauna, hakuri da juriya a harkokin su na yau da kullum kamar yadda Annabi Muhammadu ya koyar.
 “Ina farin cikin kasancewa a nan don murnar haihuwar, Wanda yafi kowa a wajen Allah wato masoyinmu Annabi Muhammad (SAW)”.inji Gawuna
 “Lokacin da Khalifan Qadiriyya ya gaya mani cewa yana gayyata ta zuwa wannan taron, nan da nan na sanar da shugabana Gwamna Ganduje wanda ya ce shi da Kan sa Zai so ya kasance a wannan taron mai albarka”.
 Ya bukaci musulmi da su ci gaba da yin koyi da koyarwar Annabi Muhammadu tare da yin kira gare su da su kasance masu kiyaye hakkoki junan su.
 Bayan yayi Kira ga al’umma dasu dage da addu’o’in Samun Zaman lafiya da cigaban kasa, Gawuna ya ba da gudummawar Naira miliyan 2 a matsayin tallafi ga wadanda suka shirya taron mauludin.
 Da yake magana da Khalifa na Harkar Qadiriyya a Afirka, Sheikh Qariballah Nasiru Kabara ya bayyana cewa makasudin taron shi ne nuna soyayya da yin tuni kan  halayen Annabi Muhammad (SAW).
 Ya yi nuni da cewa son Annabi Muhammad S A W zai kai Musulmi ga Samun Jannatul Firdaus.
 Ya nuna godiya ga Mataimakin Gwamnan Kano saboda halartar bikin mauludi.
 Tun da farko a nasa jawabin Aare Qadiriyya na Najeriya, Alh.Najimdeen Jumah ya ce alakar da ke tsakanin Kano da Abeokuta ta samo asali ne tun da dadewa ta hannun mutane irin su Marigayi Sheikh Nasiru Kabara wanda ya ba da gudummawa mai yawa ci gaban addinin Musulunci kuma ya bar abubuwan da suka wanzu kamar taron mauludi da dai Sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...