Ƴan sanda sun ceto mutum 47 daga wani gidan mari a Kano

Date:

Ƴan sanda sun ceto mutum 47 daga wani gidan mari a jihar Kano.

Gidan da ake bayyanawa da gidan gyaran hali wuri ne da iyaye kan tura ‘ya’yansu da ke muggan dabi’u da shaye-shaye da aikata manyan laifuka.

Lokacin da ‘yan sanda suka kai samame a ranar Alhamis, sun ceto mutum 47 duk maza da shekarunsu ke tsakanin 14 zuwa 35 sanye da sarkoki. Jikinsu duk dauke ya ke da alamar duka.

Kakakin ‘yan sanda Abdullahi Haruna ya shaidawa BBC cewa an cafke mutumin da ke da gidan mari kuma za a gabatar da shi a kotu.

Gwamnatin jihar dai ta haramta irin wadannan gidaje watanni 10 da suka gabata bayan kai sameme a ire-iren wadannan gidaje da ake cin zarafi ko azabtar da mutane da sunan tarbiyya.

‘Yan uwa da iyayen yara na cewa su na aike yaransu irin wadannan wurare ne saboda rashin cibiyoyin gwamnatin na gyara hali.

Mutanen da ake ceto yanzu haka na samun kulawa a asibiti.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...