Matawalle ne jagoran APC a Zamfara- MaiMala Buni

Date:

Shugaban riƙo na jam’iyyar APC ta ƙasa kuma gwamnan jihar Yobe Maimala Buni ya ce daga yau Gwamna Bello Matawalle ne jagoran jam’iyyar a jihar Zamfara.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da gwamnatin jihar Zamfara ta fitar jim kaɗan bayan komawar Matawalle APC a yau Talata.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun mai taimaka wa gwamnan na musamman kan harkokin watsa labarai Zailani Baffa, ta ambato Mai Mala na cewa: “Daga yanzu Matawalle ne jagoran jam’iyyarmu mai girma a jihar Zamfara.”

“Za ku saurari sauran shirye-shirye na samar da sabuwar jam’iyya daga wajensa nan gaba kaɗan,” in ji Buni.

A lokacin da yake karɓar tutar jam’iyyar, Gwamna Matawalle ya karɓi jagorancinta a yayin da ya ayyana kansa a matsayin mamba a cikinta.

Kazalika Gwamna Matawalle ya shiga jam’iyyar ne tare da dukkan sanatocin jihar da ke kan mulki a yanzu, da ƴan majalisar wakilan tarayya shida daga cikin bakwai da kuma dukkan ƴan majalisar dokokin jihar.

Da yake magana a wajen taron sauya sheƙar, tsohon gwaman Zamfara Abdulazeez Yari, ya ayyana goyon bayansa da kuma jajircewa don samun nasarar jam’iyyar, tare da addu’ar neman tsarin Allah daga duk wata masifa da za ta sake samun jam’iyyar.

Daga cikin waɗanda suka halarci bikin sauya shekaƙar har da gwamnonin Kano da Kaduna da Kebbi da Borno da Kogi da Neja da Yobe da Ogun da Katsina da Jigawa da kuma Filato.

Sannan tsohon gwamnan jihar Sanata Ahmad Sani Yariman Bakura ma ya halarta

62 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Dalilin da ya hana Sarki Aminu Ado Bayero zuwa gidan yari na goron dutse a yau alhamis

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin...

Matakai 3 da gwamnatin Kano ta dauka kan kafafen yada labarai a jihar

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta ce a...

Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Daga Umar Ibrahim kyarana   Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar...