Gwamnatin Jihar Kano Zata Dauki Likitoci 56 Aiki

Date:

Daga Halima A Musa


 Gwamnatin jihar Kano ta fara shirye-shiryen daukar Likitoci 56 a kokarin inganta bangaren lafiya a matakin farko a jihar nan.


 A jawabinsa yayin da yake yi wa masu neman aikin Likitancin karin haske yayin fara jarabawar gwaji da ka shiryawa Masu Neman aikin, Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Kano Dokta Tijjani Hussain ya bukaci Masu Neman aikin dasu shirya domin fuskantar kalubalen da ke gabansu .
Cikin Wata sanarwa da Jami’in Hulda da jama’a na Hukumar Maikudi Muhammad Marafa ya aikowa Kadaura24 yace Dr Hussain yana mai cewa idan Masu neman suka yi nasara za a horar da su a kan sha’anin jagoranci, Gudanar da Bayanai har ma da ayyukan Kula da Kiwon Lafiya a Matakin Farko.


 Sanarwar tace Dr Tijjani Hussain ya umarce su da su jajirce tare da sadaukar da kai lokacin da suka samu nasara a matsayin su na wadanda za su zama Ma’aikatan Hukumar Kula da Kiwon Lafiya a matakin farko ta Jiha

56 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba gaskiya a bayanin wasu Manoman Kano da suka ce Muna karbar kudi a wajensu – Civil defense

Rundunar tsaro ta Civil defense ta Kasa reshen jihar...

Korar ma’aikata a Kano: Bashir Gentile ya yiwa Faizu Alfindiki martani mai zafi

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Masanin kimiyar siyasa kuma mai sharhi...

Sakataren kungiyar NRO Abdulkadir Gude ya rasu

Allah ya yi wa dattijo, kuma Sakataren kungiyar Northern...

Gwamnatin da ta ke korar Ma’aikata ba ta Cancanci Wa’adi na biyu ba – Faizu Alfindiki

Daga  Maryam Muhammad Ibrahim   Abin takaici ne ganin yadda gwamnatin...