Gwamna Ganduje yace ya kadu da Rasuwar Shekaran Gwammaja da Tijjani Sharubutu

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf


 Gwamnan jihar Kano, Dr.Abdullahi Umar Ganduje ya nuna alhininsa dangane da rasuwar dan jam’iyyar APCn nan Ahmed Abdullahi wanda aka fi sani da Shekaran Gwammaja wanda ya rasu a Ranar Talatar data gabata Sakamakon hadarin mota.


 Gwamnan wanda Mataimakinsa Dr.Nasiru Yusuf Gawuna ya wakilta yayin da yaje gidansu Mamacin domin Yi musu ta’aziyya a Gwammaja Quarters ya ce … ” Mun shiga cikin bakin ciki da muka samu labarin rasuwar Shekaran Gwammaja.”


 “Yana daga cikin Yan gwagwarmayar matasa masu hazaka wadanda suka dukufa wajen fadakar da jama’a a kafafen yada labarai game da manufofin jam’iyyar APC da kyawawan manufofi da shirye-shiryen Gwamnatin jihar Kano. Mutuwar sa babban rashi ne ga jihar Kano da kuma  APC, saboda irin gagarumar gudummawar da yake bayarwa ga rayuwar dan adam”. Ganduje ya bayyana


 Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Mataimakin gwamnan Kano Hassan Musa Fagge ya aikowa Kadaura24 yace Gwamnan yayi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya baiwa iyalai Yan uwa da abokan Mamacin hakuri da juriya na Rashin Shekaran Gwammaja sannan kuma ya ba Jannatul Firdaus ga mamacin.


 Gwamnan ya kuma ziyarci unguwar Koki domin jajantawa dangin Alhaji Tijjani Sharubutu wanda ya rasu kwanan nan bayan fama da rashin lafiya.
 Duk da haka ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya jikansa da rahama ya bai wa iyalan juriyar rashin

290 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...