Sarkin Bichi ya yiwa Wasila Ladan Fatan samun kujerar Sakatariyar NAWOJ

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

 

Mai Martaba Sarkin Bichi Alh Nasir Ado Bayero Ofr yayi Kira da Yan jaridu da su rika bi ka’idojin aikin wajan gudanar da ayyukansu na Jarida.

Sarkin yayi kiran ne a fadarsa yayin da Shugaban Kungiyar Yan jaridu na Kasa reshe Jahar Kano Comr Abbas Ibrahim ya jagoranci tawar yan takarar kujera Sakataren Kungiyar Yan jaridu mata ta Kasa Wasila Ibrahim Ladan a fadarsa.

Talla

Alh Nasiru Ado Bayero yace Aikin Jarida aikin mai muhimmanci ga al’umma a matsayin dirka ta hudu a Gwamnati Damakaradiya, Sune suke sanar da jama’a ayyukan bangaren zartarwa da ayyukan majalisar da kuma bangaren Shari’a.

Zargin Bata Suna: Jaruma Hadiza Gabon ta Maka Wani a Kotu

Ya kuma yi fatan samun nasara ga yar takarar ta Sakataren Kungiyar mata yan jaridu ta Kasa Hajiya Wasila Ibrahim Ladan a kujera da take nema.

Wasila Ibrahim Ladan

 

A Jawabinsa Shugaban Kungiyar Yan jaridu na kasa reshe jihar Kano Com. Abbas Ibrahim yace sunzo fadar Sarkin domin gabatar da Hajiya Wasila Ibrahim Ladan a matsayi yan takarar kujera Sakataren kungiyar mata yan jaridu tare da neman albarka Sarkin.

A wani cigaban Kuma Mai Martaba Sarkin Bichi Alh Nasir Ado Bayero Ofr ya karbi bakuncin mai martaba Sarkin Funakaye dake Jahar Gombe Alh Yakubu Muhammad Kwairanga a fadar.

Sarkin na Funakaye yace yazo Fadar Sarkin ne domin jaddada zumunci wanda suka gada iyaye da kakani.

Haka zalika Mai Martaba Sarkin Bichi Alh Nasir Ado Ofr ya karbi bakuncin Shugaban shiya ta banki Jaiz bank Hajiya Na’imatu Abdullah a fadarsa,

Alh Nasir Ado Bayero ya bawa yadda banki ke gudanar da ayyukansa a tsari addini masulunci abi a yabane, yayi Kira banki ya badada ayyukansa ako ina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ƴan majalisar wakilai 2 na NNPP a Kano sun fice daga jam’iyyar zuwa APC

Wasu ‘yan majalisar wakilai biyu daga jihar Kano sun...

Wasu mutane na kokarin sayar da wata makaranta a Kano, al’ummar yankin sun nemi daukin gwamna Abba

Daga Rabi'u Usman   Al'ummar ya garin Bechi dake cikin karamar...

Gwamnatin Kano na duba yiwuwar hada kai da jami’ar Bayero don baiwa yan soshiyar midiya damar yin Difloma

Daga Isa Ahmad Getso   Gwamnatin Jihar Kano za ta duba...