Yanzu-yanzu: Kotu ta dakatar da zaben kananan hukumomin Kano

Date:

Daga Mustapha Ibrahim

 

Babbar kotun tarayya mai zamanta Kano karkashin jagorancin Mai Shari’a S. A Amobeda ta baiwa hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano wato KANSIEC umarnin dakatar da duk wasu shirye-shirye gudanar da zaben kananan hukumomin jihar da ta shirya yi a watan gobe.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito hukumar zaben ta KANSIEC ta shirya gudanar da zaben kananan hukumomin jihar kano a ranar 26 ga watan October mai zuwa.

Talla

Wani Hon. Aminu Aliyu Tiga da jam’iyyar APC ne suka shigar da karar tare da neman kotun da ta dakatar da zaben har sai ta saurari kundarin Shari’ar.

A karar da suka shigar sun kalubalanci hukumar zaben Kano kan taka ƙa’idojin shirin gudanar da zaɓe da kuma sanya kudin siyan fom ɗin shiga zaɓe, wanda APC ta hannun Hon. AA Tiga yace bai gamsu da yadda aka shirya shiga zaben ba.

El-Rufa’i ya magantu kan dawo da Sarki Sanusi II gadon sarautar Kano

Kotun ta bada umarnin dakatar da duk wani shiri na shiga zaɓen har sai an fara shari’ar.

Kotun ta kuma ce zata fara sauraren karar ne a ranar 04 ga watan October mai kamawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...

Neman Ilimin addini dana boko da sana’a ba kishiyoyin juna ba ne – Dr. Aminu Sagagi ga matasan Zango

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malamin addinin musulunci a kano...