Gwamnatin kano za ta sayo Jirage marasa matuka don yakar yan bindiga

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana shirin gwamnatin sa na siyo jirage marasa matuka da kayan aiki na sa ido da saurin mayar da martani domin kare mazauna iyakokin Kano da Katsina daga hare-haren ’yan bindiga.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

InShot 20250309 102512486

Wannan ya zo ne yayin da gwamnan ke duba shirin Joint Task Force (JTF) wajen tunkarar hare-haren kwanan nan a kananan hukumomin Tsanyawa da Shanono, inda aka sace mutane kimanin 5 a Tsanyawa da 10 a Shanono, ciki har da mace guda da ta rasa rayuwarta.

Matsalar tsaro: Tinubu ya turo tawagar Jami’an tsaro ta musamman Kano – Gwamna Abba

Gwamna ya roki mazauna yankunan da su ba da bayanai masu amfani kan motsin ’yan bindiga, sannan ya umarci JTF da su yi iyakar ƙoƙarinsu wajen kubutar da wadanda aka sace.

Ya tabbatar wa dakarun da iyalan da abin ya shafa cewa gwamnati na yin iyakar ƙoƙarin ta wajen mayar da wadanda aka sace ga iyalansu cikin kankanin lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...